Al-Muddaththir

المدثر

The Cloaked One56 ayahsMeccan

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

يَٰٓأَيُّهَا ٱلۡمُدَّثِّرُ﴿١

1Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.

قُمۡ فَأَنذِرۡ﴿٢

2Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi

وَرَبَّكَ فَكَبِّرۡ﴿٣

3Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,

وَثِيَابَكَ فَطَهِّرۡ﴿٤

4Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,

وَٱلرُّجۡزَ فَٱهۡجُرۡ﴿٥

5Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.

وَلَا تَمۡنُن تَسۡتَكۡثِرُ﴿٦

6Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri

وَلِرَبِّكَ فَٱصۡبِرۡ﴿٧

7Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure

فَإِذَا نُقِرَ فِي ٱلنَّاقُورِ﴿٨

8To, idan aka yi bũsa a cikin ƙaho.

فَذَٰلِكَ يَوۡمَئِذٖ يَوۡمٌ عَسِيرٌ﴿٩

9To, wannan, a rãnar nan, yini ne mai wuya

عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ غَيۡرُ يَسِيرٖ﴿١٠

10A kan kãfirai, bã mai sauƙi ba ne.

ذَرۡنِي وَمَنۡ خَلَقۡتُ وَحِيدٗا﴿١١

11Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai,

وَجَعَلۡتُ لَهُۥ مَالٗا مَّمۡدُودٗا﴿١٢

12Kuma Na sanya masa dũkiya shimfiɗaɗɗiya

وَبَنِينَ شُهُودٗا﴿١٣

13Da ɗiyã halartattu,

وَمَهَّدتُّ لَهُۥ تَمۡهِيدٗا﴿١٤

14Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.

ثُمَّ يَطۡمَعُ أَنۡ أَزِيدَ﴿١٥

15Sa'an nan, yanã kwaɗayin in yi masa ƙãri!

كَلَّآۖ إِنَّهُۥ كَانَ لِأٓيَٰتِنَا عَنِيدٗا﴿١٦

16Faufau! Lalle ne, shĩ yã kasance, ga ãyõyin Mu, mai tsaurin kai.

سَأُرۡهِقُهُۥ صَعُودًا﴿١٧

17Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.

إِنَّهُۥ فَكَّرَ وَقَدَّرَ﴿١٨

18Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da Alƙur'ãni)

فَقُتِلَ كَيۡفَ قَدَّرَ﴿١٩

19Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.

ثُمَّ قُتِلَ كَيۡفَ قَدَّرَ﴿٢٠

20Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.

ثُمَّ نَظَرَ﴿٢١

21Sa'an nan, ya yi tunãni

ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ﴿٢٢

22Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.

ثُمَّ أَدۡبَرَ وَٱسۡتَكۡبَرَ﴿٢٣

23Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,

فَقَالَ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ يُؤۡثَرُ﴿٢٤

24Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."

إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا قَوۡلُ ٱلۡبَشَرِ﴿٢٥

25"Wannan maganar mutum dai ce."

سَأُصۡلِيهِ سَقَرَ﴿٢٦

26Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا سَقَرُ﴿٢٧

27Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!

لَا تُبۡقِي وَلَا تَذَرُ﴿٢٨

28Bã ta ragẽwa, kuma bã ta bari.

لَوَّاحَةٞ لِّلۡبَشَرِ﴿٢٩

29Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).

عَلَيۡهَا تِسۡعَةَ عَشَرَ﴿٣٠

30A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.

وَمَا جَعَلۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَٰٓئِكَةٗۖ وَمَا جَعَلۡنَا عِدَّتَهُمۡ إِلَّا فِتۡنَةٗ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ لِيَسۡتَيۡقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَيَزۡدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِيمَٰنٗا وَلَا يَرۡتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ وَٱلۡكَٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَمَا يَعۡلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَۚ وَمَا هِيَ إِلَّا ذِكۡرَىٰ لِلۡبَشَرِ﴿٣١

31Kuma ba Mu sanya ma'abũta wutã (wãto matsaranta) ba, fãce malã'iku, kuma ba Mu sanya adadinsu (gõma sha tara) ba, fãce dõmin fitina ga waɗanda suka kãfirta domin waɗanda aka bai wa littãfi su sãmi yaƙĩni kuma waɗanda suka yi ĩmãni su ƙãra ĩmãni, kuma waɗanda aka bai wa littãfi da mũminai bã zã su yi shakka ba, kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kãfirai su ce: "Mẽ Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misãli?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce ga mutum.

كَلَّا وَٱلۡقَمَرِ﴿٣٢

32A'aha! Ina rantsuwa da watã.

وَٱلَّيۡلِ إِذۡ أَدۡبَرَ﴿٣٣

33Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.

وَٱلصُّبۡحِ إِذَآ أَسۡفَرَ﴿٣٤

34Da sãfiya idan ta wãye.

إِنَّهَا لَإِحۡدَى ٱلۡكُبَرِ﴿٣٥

35Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.

نَذِيرٗا لِّلۡبَشَرِ﴿٣٦

36Mai gargaɗĩ ce ga mutum.

لِمَن شَآءَ مِنكُمۡ أَن يَتَقَدَّمَ أَوۡ يَتَأَخَّرَ﴿٣٧

37Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabãta ko ya jinkirta.

كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا كَسَبَتۡ رَهِينَةٌ﴿٣٨

38Kõwane rai ga abin da ya aikata jingina ce.

إِلَّآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡيَمِينِ﴿٣٩

39Fãce mutãnen dãma.

فِي جَنَّٰتٖ يَتَسَآءَلُونَ﴿٤٠

40A cikin Aljanna suna tambayar jũna.

عَنِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ﴿٤١

41Game da mãsu laifi.

مَا سَلَكَكُمۡ فِي سَقَرَ﴿٤٢

42(Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar?"

قَالُواْ لَمۡ نَكُ مِنَ ٱلۡمُصَلِّينَ﴿٤٣

43Suka ce: "Ba mu kasance munã a cikin mãsu salla ba."

وَلَمۡ نَكُ نُطۡعِمُ ٱلۡمِسۡكِينَ﴿٤٤

44"Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalautã ba."

وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلۡخَآئِضِينَ﴿٤٥

45"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."

وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ﴿٤٦

46"Mun kasance munã ƙaryata rãnar sãkamako."

حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلۡيَقِينُ﴿٤٧

47"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."

فَمَا تَنفَعُهُمۡ شَفَٰعَةُ ٱلشَّٰفِعِينَ﴿٤٨

48Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.

فَمَا لَهُمۡ عَنِ ٱلتَّذۡكِرَةِ مُعۡرِضِينَ﴿٤٩

49Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.

كَأَنَّهُمۡ حُمُرٞ مُّسۡتَنفِرَةٞ﴿٥٠

50Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.

فَرَّتۡ مِن قَسۡوَرَةِۭ﴿٥١

51Sun gudu daga zãki.

بَلۡ يُرِيدُ كُلُّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ أَن يُؤۡتَىٰ صُحُفٗا مُّنَشَّرَةٗ﴿٥٢

52A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa) ana wãtsãwa

كَلَّاۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلۡأٓخِرَةَ﴿٥٣

53A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.

كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذۡكِرَةٞ﴿٥٤

54A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ﴿٥٥

55Dõmin wanda ya so, ya tuna.

وَمَا يَذۡكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ هُوَ أَهۡلُ ٱلتَّقۡوَىٰ وَأَهۡلُ ٱلۡمَغۡفِرَةِ﴿٥٦

56Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.

RELATED SURAHS